Zan
Canja Jiha Muddin Ba Za’a Kula Da Mu -------Dan Gudun Hijira
Daga
Rabilu Abubakar, Gombe
Wani xan gudun Hijirar Talala dake yanki Buni Yadi,
Alhaji Ari Talala ya bayyana cewa shi kan a shirye yake da ya canja jiha ya
zama dan Gombe tunda shugabanin da suka zaba basa tausayawa irin halin da suke
ciki na quncin rayuwa.
Alhaji Ari Talala, ya bayyana hakan ne a lokacin da
yake zantawa da wakilinmu a Gombe inda yace sun sa kuri’a sun zave Sanatansu Ali
Ndume da yar Majalisar tarayya Asabe Bileta kuma sun zavi shugaban qasa
Muhammadu Buhari, amma anqi kulawa dasu an barsu a suna ta gudun hijira.
Yace shi kan zai iya canja jiha yabar Dajin da suke
xin nan saboda babu hanya kuma har yanzu akwai Maharan nan na Boko Haram a
wajen saboda haka a xauki matakin farko na samar da hanya da zai kawo qarshen
wadannan mutane.
Dan gudun hijirar ya qara da cewa zamansu a wannan
Jeji na Talala ba zai kai su ba saboda
idan ba’a san yadda za’ayi a kawar da waxannan Yaran ba babu yadda za’ayi su
koma wannnan gari su zauna.
Ari Kaku, ya kuma ce garuruwan da suke wannan yanki
na Talala da Ajigin da Gwargore da Kaba nan ne Yan Boko Haram din suka dawo
bayan tarwatsasu da akayi daga Dajin Sambisa.
A cewarsa abunda yasa yake cewa zai canja jiha shi
ne saboda shugabanin da suka zaba babu wanda ya taba zuwa ya nemesu a Gombe da
suke gudun hijira don ya taimakesu amma da buqatarsu ta taso na neman kuri’u ai
har inda suke xin a Gombe aka turo motoci aka xaukeso suka je sukayi zave amma
yanzu an manta dasu.
“Muna
fama da matsalar tsadar rayuwa da kuxin gidan haya ga babu sana’a muna fama da
quncin rayuwa kuma anqi a kula damu ai dole ma ranmu zai vaci saboda ba’a xauke
mu muna da amfani ba, “inji Ari Kaku.
Daga nan sai ya yi kira ga gwamnonin jihohin Borno
da Yobe da cewa su haxa kai suyi dukkan mai yiwuwa wajen ganin sun mayar da duk
wani xan gudun hijira inda ya fito tunda yanzu an fara samun zaman lafiyar da
ake ganin zai dore.
Xxx