BUDADDIYAR WASIKA
KIRA GA MA SHAYA TABA SIGARI
Biyo bayan sanarwar da kamafonin da suke Sarrafa Taba Sigari, su ka yi wa jama’a na fada masu cewar ita wannan Tabar Ma’aikatar kiwon Lafiya ta kasa ta yi gargadin cewar shanta hatsari ne ga rayuwa kuma mashayanta suna iya mutuwa tun da kuruciyarsu, sannan aka lika a jikin kwalin Tabar amma duk da haka muka ki ji wajen yin kunnen uwar shegu na saya da kudin mu, mu sha.
Da wannan sanarwa da kamfanonin da suke sarrafa Tabar suka yi na ke son in dauki wannan damar wajen yin kira ga dukkan daukacin jama’a da sukan sha Taba Sigari, a bayynar jama’a da cewar su dai na domin bai dace ba saboda wanda baya shan Tabar idan ka busa ma shi hayakin Tabar za ta cutar da shi kuma ka dauki alhakinsa wajen cutar da lafiyar sa.
Sannan kuma ina son in kirayi gwamnati da babbar murya wajen daukar nauyin fadakar da masha ya Taba Sigari, ko a Jaridu ko a gidajen Radiyo, ko a Talabijin ne cewar dukkan mai shan Taba ya kaurace gefe guda domin shan ta a cikin jama’a akwai cutarwa, ga wadanda ba sa sha amma duk wanda ya yi kunnen uwar shegu da wannan sanarwa sai gwamnati ta hukunta shi.
Har yanzu kuma kamar wadanda suke tafiya suna shan Tabar a kan hanya hakan bai dace ba domin a tafiyar da kake yi din za ka iya wuce wani a daidai lokacin da ka busa hayakin nan ka ga ka busa ma shi, kuma ai kamar yadda mutum ba zai dinga tafiya yana cin abinci ba to ta ya ya zai dinga tafiya ya na shan Taba, ai hakan ma zai kara zubar masa da mutunci a idon jama’a.
Ina kuma so in sake kira ga gwamnatin tarayya na cewar ta yi dukkan mai yi wuwa wajen ganin ta magance wannan matsala ta Shan Taba a cikin jama’a duk da cewar mai shan Taba da zarar ka fa da masa cewar shan Taba babu kyau zai fara ce maka ai Likitoci ma suna Sha, abin tambaya a nan shine don Likita yana shan Taba shi kenan sai kai ma ka sha Taba,? ko kuma ka ji mutum yace maka ai ba haram bace almumbazzaranci ne, almumbazzaranci abin yi ne, ga musulmi ai Addinin Musuluci ya fada mana cewar dukkan almubazzari abokin Shaidan ne to wa yake so ya zama abokin Shaidan.
Ma’aikatan Lafiya, sun tabbatar da cewa wanda ba ya shan Taba Sigari, idan mai shan ta, ya busa ma shi hayakin shi wanda ba ya sha din yafi cutuwa da illar ita Taba din.
Abin tambaya ma a nan shine menene ya sa jama’a ba za su kiyaye lafiyar su ba, tunda su kansu kamfanonin da suka yi yo Tabar nan sun fada cewar ta na da hatsarin gaske ga rayuwa amma muke shan ta, ba fa abinci bace ko kuma ibada bace ba balle muce ta zama mana dole sai mun sha?.
Ni dai fata na a nan shine na riga nasan babu yadda za’a yi adai na shan Taba Sigari, amma abin roko shine adaina shanta a cikin jama’a ko kuma shanta barkatai a wuraren da ba su dace ba, sai dai muna fatan tunda shan Taba hatsari ce ga rayuwa, Allah ya kawo karshen shan ta ga jama’a tunda ba magani ba ce don ka sha kace za ta maka maganin ciwon kai ko ciwon ciki ko ma kace za ta hana ka jin yunwa, in kuma ba haka ba to ina fata Allah ya sa masu shan ta su san cewa ba ta da wani amfani ga rayuwarsu sai ma lalatar masu jiki su yi bagi ga bakin baki sannan kuma ga rage masu daraja da kima a idon jama’a.
End.
Daga ABUBAKAR RABILU, Bolari Gombe
G.S.M 080-36597674, 080-28094624
I mail: - rabiluabubakar@yahoo.
No comments:
Post a Comment