Friday, October 27, 2023

 Gombe Revenue Tribunal Generates N12 Billion Within A Year 


From Rabilu Abubakar, Gombe

The Gombe State Revenue Recovery Tribunal has generated N12 billion within a year as revenue to the state government.

Chairman of the revenue recovery tribunal His Workship Muhammad Tukur Jungudo stated this during the commemoration of one year anniversary of the tribunal.

He explained that the tribunal was established last year on the 5th of October 2022 with the mandate to recover government's revenues from companies and individuals.

Jungudo, noted that the aim of the tribunal is to surmount the problems of tax evasion which causes government to lose a lot of incomes and to ensure fairness and transparency in the tax system.

He said another objective is enhancing tax payers' confidence and curtailing delays and bottlenecks in the adjudication of tax matters at conventional courts.

He therefore said with the establishment of this tribunal, the revenue of Gombe state has risen, which shows that from October to December 2022 the state revenue has risen to N6.6 billion and also from January to September 2023 to N12 billion.

In his remarks during the commemoration ceremony, Governor Muhammad Inuwa Yahaya represented by his deputy Manasseh Jatau said experience has shown that all over the world, revenue is a crucial element in the running of government.

He pointed out that various empires, kingdoms now and before colonial era, there were people saddled with the responsibility of collecting revenues in the society adding that tax payers should be paying their dues as at when due in order to enable government deliver dividends of democracy.

"While the drive for revenue generation, collection and utilization have been the magnet towards which leaders are attracted to the administration under the transparent, accountable, and good governance of his excellency Muhammad Inuwa Yahaya, he saw the compelling need to set up the Gombe State Revenue Recovery Tribuna.", he stated.

He therefore said records available indicates that this is the first of such in the entire North east geo political zone.

Yahaya, admitted that before the establishment of the tribunal, the state's revenue stood at N10.6 billion, but increased to N18.9 billion after the establishment.

Saturday, April 10, 2021

Gombe govt encouraging irrigation to overcome threats to food security

 Gombe govt encouraging irrigation to overcome threats to food security


From. Rabilu Abubakar, Gombe

The Gombe state governor Muhammad Inuwa Yahaya, said his administration was encouraging irrigation farming as a way of overcoming the threat to food security bedveling the Nation.

Governor Inuwa, who was represented by his deputy Manasseh Daniel Jatau, in a one day explortory dialogue of the United Nation system summit in the north east held in Gombe yesterday on food and nutrition. 

Saying with the Dams in Dadin-kowa, Balanga and Cham in Gombe state government would continue utilize them and improved agriculture towards tackling food security.

He also said since nutrition was one of the major challenges facing  the state, there was the need for collaboration between the state government and other agencies towards tackling the issue.

In his goodwiil message the representative of USAID, Dr Farouk Kurawa, said it was a known fact that the sustained humanitarian crisis in North East for over a decade had contributed significantly to high burden of poverty and hunger among vulnerable population in the region.

Said this was worsened by the Covid 19 pandemic, which clearly showed the weakness in our entire system and the need to strengthen collaboration and plans to address these gaps.

Dr Kurawa, added that hunger and poverty continue to be an issue we are facing due to an ever-growing population without a corresponding increase in the food production the height of insecurity in most part of the North East, hence the meeting would help address the challenge of hunger.

End.

Wednesday, April 25, 2018

Yau za'a fara sauraron ra'ayoyin jama'a kan batun karin albashi na shiyar arewa maso gabas a Gombe.


Yau za'a  fara sauraron ra'ayoyin jama'a kan batun karin albashi na shiyar arewa maso gabas a Gombe.

By Rabilu Abubakar, Gombe

A yau Alhamis ne Kwamitin da shugaban Najeriya Muhammadu Buhari, ya kafa dan sauraron ra'ayoyin jama'a game da karin mafi karancin albashi zai fara sauraron ra'ayoyi jama'a na shiyar arewa maso gabas a Gombe.

kwamitin karkashin jagorancin mataimakin shugaban kungiyar gwadago ta kasa NLC Mista James Peter Adeyemi da taimakon shugaban kungiyar gwadagon na jihar Gombe.

taron jin ra'ayoyin jama'ar zai gudana ne a babban otel din nan na kasa da kasa dake Gombe inda ake sa ran gwamnonin jihohin arewa maso gabas da kungiyoyin lauyoyi da na ma'aikata da sauran su za su halarta har ma da daidaikun jama'ar gari.

ku biyo mu dan jin yadda taron zai kasance.

Monday, July 3, 2017

A yau Litinin 3 ga watan Yuli 2017 Allah ya yiwa Alhaji Yusuf Maitama Sule Dan Masanin Kano Kano Rasuwa a wani asibiti a kasar Cairo.

za'ayi Jana'izar sa gobe da misalin karfe 2:00pm na rana in Allah ya kai mu a Kano.

za mu kawo muku cikakken bayani da tarihin sa nan gaba 

Thursday, January 19, 2017




Zan Canja Jiha Muddin Ba Za’a Kula Da Mu -------Dan Gudun Hijira

Daga Rabilu Abubakar, Gombe

Wani xan gudun Hijirar Talala dake yanki Buni Yadi, Alhaji Ari Talala ya bayyana cewa shi kan a shirye yake da ya canja jiha ya zama dan Gombe tunda shugabanin da suka zaba basa tausayawa irin halin da suke ciki na quncin rayuwa.

Alhaji Ari Talala, ya bayyana hakan ne a lokacin da yake zantawa da wakilinmu a Gombe inda yace sun sa kuri’a sun zave Sanatansu Ali Ndume da yar Majalisar tarayya Asabe Bileta kuma sun zavi shugaban qasa Muhammadu Buhari, amma anqi kulawa dasu an barsu a suna ta gudun hijira.

Yace shi kan zai iya canja jiha yabar Dajin da suke xin nan saboda babu hanya kuma har yanzu akwai Maharan nan na Boko Haram a wajen saboda haka a xauki matakin farko na samar da hanya da zai kawo qarshen wadannan mutane.

Dan gudun hijirar ya qara da cewa zamansu a wannan Jeji na Talala ba zai kai    su ba saboda idan ba’a san yadda za’ayi a kawar da waxannan Yaran ba babu yadda za’ayi su koma wannnan gari  su zauna.

Ari Kaku, ya kuma ce garuruwan da suke wannan yanki na Talala da Ajigin da Gwargore da Kaba nan ne Yan Boko Haram din suka dawo bayan tarwatsasu da akayi daga Dajin Sambisa.

A cewarsa abunda yasa yake cewa zai canja jiha shi ne saboda shugabanin da suka zaba babu wanda ya taba zuwa ya nemesu a Gombe da suke gudun hijira don ya taimakesu amma da buqatarsu ta taso na neman kuri’u ai har inda suke xin a Gombe aka turo motoci aka xaukeso suka je sukayi zave amma yanzu an manta dasu.

“Muna fama da matsalar tsadar rayuwa da kuxin gidan haya ga babu sana’a muna fama da quncin rayuwa kuma anqi a kula damu ai dole ma ranmu zai vaci saboda ba’a xauke mu muna da amfani ba, “inji Ari Kaku.

Daga nan sai ya yi kira ga gwamnonin jihohin Borno da Yobe da cewa su haxa kai suyi dukkan mai yiwuwa wajen ganin sun mayar da duk wani xan gudun hijira inda ya fito tunda yanzu an fara samun zaman lafiyar da ake ganin zai dore.



Xxx

Sunday, February 2, 2014

INA SHARE KWANAKI UKU BA CI BA SHA A ZAMANA NA GIDAN YARI----MANJO AL-MUSTAPHA



INA SHARE KWANAKI UKU BA CI BA SHA A ZAMANA NA GIDAN YARI----MANJO AL-MUSTAPHA

Daga Rabilu Abubakar, a Gombe

Tsohon dogarin tsohon shugaban qasar Najeriya Manjo Hamza Al-Mustapha wanda ya shafe shekaru goma sha biyar yana zaman gidan kurkuku a qasar nan ya bayyana irin yadda zamansa a gidan kurkukun ya kasance cikin azabar da   ya sha game da zama da ishiruwa da yunwa.

Manjo Al-Mustapha, ya bayyana cewa yana zama na wasu kwanaki da basu gaza uku ko huxu ba ba tare da an bashi abinci ko ruwan sha ba har ya gama zamansa na gidan kurkuku ya fito.

Manjo Hamza Al- Mustapha, wanda shine jagoran wata qungiya mai suna AFUDY ya bayyana hakan ne a lokacin da ya zo jihar Gombe don jaddada muhimmancin wannan qungiya ta sa mai suna AFUDY wacce yace ya kafata ne don samarwa da matasa aikin yi a faxin qasar nan.

Manjo Al-Mustapha, yace tun bayan fitowarsa daga gidan yari a ranar 12 ga watan Yuni na shekara ta 2013 yake yawo don zaga jihohin qasar nan wajen ganin ya gana da masu ruwa da tsaki don shaida musu aniyar sa ta ceto qasar nan daga halin da take ciki musammam ma yankinsa da ya fito na arewa maso gabas wanda yake qoqarin ganin ya ceto matasan yankin.

Ya kuma ce kafin a tsare shi a gidan yarin shekaru goma sha biyar da suka gabata yana yawo ba dare ba rana yana zaga qasar nan saboda yana aiki da qungiyoyi masu yawa kama daga kudancin Najeriya har zuwa arewaci don ganin an ceto matasa.

A cewar sa a shekara ta 1984 ne yasa kansa a cikin wata qungiya inda suke faxi tashin ganin sun taimakawa waxanda suke da buqatar hakan wanda burinsu shine na ganin an samu al’umma wacce take da tarbiyaa da xa’a wacce ba za’a sameta da rikici na tashe-tashen hankula ba wanda a lokacin da aka kamashi aka tsare shine wasu qungiyoyin sun tsaya amma yanzu da ya fito shine yake ci gaba.

 Manjo Hamza Al-Mustapha, ya kuma xan bada bayani halin quncin rayuwar da ya shiga a gidan Yarin na rashin samun abinci da ruwan sha wanda sai ya yi kwanaki sannan a ba shi sau xaya. Amma a cewar sa akwai wani Soja xan asalin jihar wanda yake taimaka masa da ruwa da abinci a boye amma Allah ya yi masa rasuwa a wani lokaci da yaje nemo masa qosai da ruwa.

A boye wannan sojan yake tsallakewa ya fita da Babur xinsa ya nemo min ruwan leda na Pure water da abinci wata rana da qosai ya kawo min inci ba tare da an ganshi ba” inji Al-Mustapha.

Cikin jimami da qarfin zuciya Al-Mustapha, yace ranar da wannan Soja zai rasu yazo ya gaishe shi yace Oga bari inje in nemo maka abinci bayan munyi sallama dashi ya fita yaje ya nemo min qosai da ruwa akan babur xinsa yana dawowa sai ya yi hatsari yaji ciwo kafin ayi masa allura tetanus ya shiga wanda shine ya yi sanadiyar ajalinsa

 Daga nan ne sai yace bayan hidimar wannan qungiya tasa taimakon iyalan wannan Soja suna daga cikin dalilansa na zuwa Gombe don ya taimakawa iyalan wannan Soja bisa yadda ya dinga masa hidima da har kan ya zamo sanadiyar rayuwar sa.

            

Xxx

Alhaji Salisu Muhammad Gombe shugaban kungiyar Izala ta Gombe kuma Sakataren tsare-tsare na kungiyar yan Agajin Izala ta kasa tare da Babban Sakataren kungiyar yan agajin ta kasa Alhaji Abba Katsina a wajen taron Majalisar yan agajin na kasa a jihar Gombe a ranar Asabar 1 ga watan Janairu 2014 wanda ya dauki hoto Abubakar Rabilu.