Sunday, February 2, 2014

INA SHARE KWANAKI UKU BA CI BA SHA A ZAMANA NA GIDAN YARI----MANJO AL-MUSTAPHA



INA SHARE KWANAKI UKU BA CI BA SHA A ZAMANA NA GIDAN YARI----MANJO AL-MUSTAPHA

Daga Rabilu Abubakar, a Gombe

Tsohon dogarin tsohon shugaban qasar Najeriya Manjo Hamza Al-Mustapha wanda ya shafe shekaru goma sha biyar yana zaman gidan kurkuku a qasar nan ya bayyana irin yadda zamansa a gidan kurkukun ya kasance cikin azabar da   ya sha game da zama da ishiruwa da yunwa.

Manjo Al-Mustapha, ya bayyana cewa yana zama na wasu kwanaki da basu gaza uku ko huxu ba ba tare da an bashi abinci ko ruwan sha ba har ya gama zamansa na gidan kurkuku ya fito.

Manjo Hamza Al- Mustapha, wanda shine jagoran wata qungiya mai suna AFUDY ya bayyana hakan ne a lokacin da ya zo jihar Gombe don jaddada muhimmancin wannan qungiya ta sa mai suna AFUDY wacce yace ya kafata ne don samarwa da matasa aikin yi a faxin qasar nan.

Manjo Al-Mustapha, yace tun bayan fitowarsa daga gidan yari a ranar 12 ga watan Yuni na shekara ta 2013 yake yawo don zaga jihohin qasar nan wajen ganin ya gana da masu ruwa da tsaki don shaida musu aniyar sa ta ceto qasar nan daga halin da take ciki musammam ma yankinsa da ya fito na arewa maso gabas wanda yake qoqarin ganin ya ceto matasan yankin.

Ya kuma ce kafin a tsare shi a gidan yarin shekaru goma sha biyar da suka gabata yana yawo ba dare ba rana yana zaga qasar nan saboda yana aiki da qungiyoyi masu yawa kama daga kudancin Najeriya har zuwa arewaci don ganin an ceto matasa.

A cewar sa a shekara ta 1984 ne yasa kansa a cikin wata qungiya inda suke faxi tashin ganin sun taimakawa waxanda suke da buqatar hakan wanda burinsu shine na ganin an samu al’umma wacce take da tarbiyaa da xa’a wacce ba za’a sameta da rikici na tashe-tashen hankula ba wanda a lokacin da aka kamashi aka tsare shine wasu qungiyoyin sun tsaya amma yanzu da ya fito shine yake ci gaba.

 Manjo Hamza Al-Mustapha, ya kuma xan bada bayani halin quncin rayuwar da ya shiga a gidan Yarin na rashin samun abinci da ruwan sha wanda sai ya yi kwanaki sannan a ba shi sau xaya. Amma a cewar sa akwai wani Soja xan asalin jihar wanda yake taimaka masa da ruwa da abinci a boye amma Allah ya yi masa rasuwa a wani lokaci da yaje nemo masa qosai da ruwa.

A boye wannan sojan yake tsallakewa ya fita da Babur xinsa ya nemo min ruwan leda na Pure water da abinci wata rana da qosai ya kawo min inci ba tare da an ganshi ba” inji Al-Mustapha.

Cikin jimami da qarfin zuciya Al-Mustapha, yace ranar da wannan Soja zai rasu yazo ya gaishe shi yace Oga bari inje in nemo maka abinci bayan munyi sallama dashi ya fita yaje ya nemo min qosai da ruwa akan babur xinsa yana dawowa sai ya yi hatsari yaji ciwo kafin ayi masa allura tetanus ya shiga wanda shine ya yi sanadiyar ajalinsa

 Daga nan ne sai yace bayan hidimar wannan qungiya tasa taimakon iyalan wannan Soja suna daga cikin dalilansa na zuwa Gombe don ya taimakawa iyalan wannan Soja bisa yadda ya dinga masa hidima da har kan ya zamo sanadiyar rayuwar sa.

            

Xxx

Alhaji Salisu Muhammad Gombe shugaban kungiyar Izala ta Gombe kuma Sakataren tsare-tsare na kungiyar yan Agajin Izala ta kasa tare da Babban Sakataren kungiyar yan agajin ta kasa Alhaji Abba Katsina a wajen taron Majalisar yan agajin na kasa a jihar Gombe a ranar Asabar 1 ga watan Janairu 2014 wanda ya dauki hoto Abubakar Rabilu.

KUNGIYAR IZALA TA GUDANAR DA TARON MAJALISAR ‘YAN AGAJIN TA NA QASA A GOMBE



QUNGIYAR IZALA TA GUDANAR DA TARON MAJALISAR ‘YAN AGAJIN TA NA QASA A GOMBE

Daga Rabilu Abubakar, a Gombe

A makon nan ne qungiyar ‘yan agajin jama’atu Izalatul Bidi’ah wa’iqamatussunah ta gudanar da taron majalisar ‘yan agajin ta na qasa a jihar Gombe don tattauna matsalolin da suka shafi qungiyar.

Da yake yiwa manema labarain qarin haske kan maqasudin wannan taro babban Daraktan ‘yan agajin na qasa Injiniya Mustapha Imam Sitti, cewa ya yi qungiyar  ‘yan agajin Izala takan gudanar da irin wannan taro ne don shawo kan matsalolin da suka shafi qungiya da kuma irin ayyukan da zasu fuskanta a gaba.

Injiniya Mustapha Sitti, yace a lokacin irin wannan taro sukan faxakar da ‘yan agajinsu yadda zasu kula da maras lafiya a asibiti idan sun kai xauki  da kuma yadda za su bai wa wanda ya gamu da hatsarin mota agajin gaggawa da kuma bada tallafi a lokacin da aka samu hatsarin gobara.

A cewar sa a shekarar da ta gabata sun gudanar da irin waxannan ayyuka shi yasa yanzu suka sake taruwa don suga irin nasarorin da suka samu sannan su ga irin tsare-tsaren da za suyi a wannan shekara ta 2014.

Daraktan ‘yan agajin ya qara da cewa qungiyarsu ta ‘yan agaji sukan gudanar da irin wannan taro ne sau uku ko sau huxu a kowacce shekara sannan kuma su kan  gudanar da tarurruka na qarawa juna sani don qara karantar da mambobin  qungiyar  tasu ta ‘yan agaji don su sami makamar aiki da suke gudanarwa  a cikin wannan qasa.
  
Mustapha Sitti, ya kuma ce wannana qungiya ta ‘yan agaji ta samu nasarori da dama wanda babban nasarar da suka samu ita ce mutane suna fahimtar aikin da suke yi domin ko a lokacin aikin hajji hankalin jama’a bai kwanciya har sai sunga ‘yan agajin sannan suke bari a fara tantancesu a filin jirgin sama.

Ya kuma ce bama anan qasa Najeriya wannan qungiya tasu take aiki ba hatta a qasashe irinsu Saudi Arebiya da Benin da Ghana da Kamaru wannan qungiya ta kafu kuma tana taimakawa kuma a shekarar da ta gabata ma sunje har Saudi arebiya sunyi miti na qungiyar  wanda har gwamnatin qasar ta fahimci irin wa’azuzzukan da qungiyar take gabatarwa.

Injiniya Mustapha Sitti, ya nuna takaicinsa na rashin samun tallafi da qungiyar ‘yan agajin bata samu a lokacin da ya kamata musammam ma na kujerun aikin hajji da za su bai wa ‘yan agajinsu don taimakon Alhazai a can qasar Saudiya, inda yace da kamar yadda kowacce qasa da gwamnati take taimakawa Red Cross  haka ake taimakawa ‘yan agajin da basu da matsala.

Daga nan sai yace babban burin qungiyar a wannan shekarar shine suga ayyukansu sun qara faxaxa ta kowacce hanya don taimakon al’ummar musulmi.

Shi kuwa da yake tsokaci shugaban qungiyar izala ta jihar Gombe wanda kuma shine babban sakataren tsare-tsare na qungiyar ‘yan agaji ta qasa Alhaji Salisu Muhammad Gombe, godewa shugabannin qungiyar ya yi na yadda suka zavi jihar Gombe don gudanar da wannan taro.

Xxx

Sunday, January 26, 2014

IDAN SANATAN MU DANJUMA GOJE YA KOMA APC ZAMU AIKA TAKARDA MU DAWO DASHI----INJI Yayari



Fagen Siyasa

IDAN SANATAN MU DANJUMA GOJE YA KOMA APC ZAMU AIKA TAKARDA MU DAWO DASHI----INJI Yayari

Daga Rabilu Abubakar, Gombe

Alhaji Ahmad Yayari, Shugaban ma’aikata ne na gidan gwamnatin jihar Gombe kuma dan asalin garin Chilo a karamar hukumar Akko, shi ya bayyana cewa da zarar Sanatan yankinsu Alhaji Muhammad Danjuma Goje, ya kuskura ya canja shega daga jam’iyyar PDP da aka zabe shi ya koma jam’iyyar adawa ta APC za su tura ya dawo domin basu yake wakilta ba.

Alhaji Ahmad Yayari, ya bayyana hakan ne a lokacin da yake gabatar da jawabinsa a garin Kumo helkwatar karamar hukumar Akko a yayin da gwamnan jihar Alhaji Ibrahim Hassan Dankwambo, yake rangadin ziyartar mazabun Sanatoci uku (Senatorial Tour)

A bayanan Ahmad Yayari, wanda tsohon Kwamishina ne har tsawon shekaru takwas a tsohowar gwamnatin da ta gabatan ya shaidawa gwamna Dankwambo cewa su al’ummar Gombe ta tsakiya musammam mutane garin Kumo basu amfana da romon democradiyya a gwamnatin baya ba domin duk girman garin Kumo babu aikin naira miliyan goma  a shekaru takwas din da gwamnatin tayi.

Ya kuma ce koda hanyar mararabar Zambuk zuwa Lubo da Hinna zuwa Gwani, a yankin Yamaltu Deba duk wash-wash ne akayi yanzu ya kirayi gwamna Dankwambo da cewa ya sake su domin dai dai suke da ba’ayi ba.

Shugaban ma’aikatan ya kara tabbatarwa gwamana Dankwambo cewa su mutanen Gombe ta tsakiya jam’iyyar PDP suke yi kuma tsohowar ta Bamanga Tukur, ba sabuwar ba amma Sanatan su da suka zaba Alhaji Danjuma Goje, ya tashi a gaban duniya yace shi dan sabuwar PDP ne wanda su idan dai a sabuwar PDP yake basu yake wakilta ba.

“ Yanzu haka muna jin rade-radin cewa zai koma jam’iyyar Hadaka wacce aka yi hadin gambiza ta APC  idan ya koma bamu yake wakilta ba don haka gwamna ka sani amma daga ranar da muka ji ya koma APC din mu al’ummar mazabar Gombe ta tsakiya kamar yadda muka kai shi haka zamu dawo dashi” inji Yayari.

Ya ci gaba da cewa yanzu lokaci bai zo tukuna amma yace suna jira suga ranar da zai koma APC din sannan kuma ya kara da cewa mutanen Gombe ta tsakiya sun gaya masa cewa kar ya yi Magana ya zuba ido kawai ya yi kallo suna jira suka wanda zai bada gidansa ko ofis a kafa ofishin sabuwar jam’iyyar ta APC.

Shi kuwa Kakakin Majalisar Dokoki ta jihar Gombe Alhaji Inuwa Garba, wanda yake wakiltar Yamaltu ta yamma cewa ya yi su mutanen yankin Yamaltu Deba wanda take Gombe ta tsakiya bakinsu daya da mutane Akko basa wata sabuwar jam’iyya in ba PDP ba.

Alhaji Inuwa Garba, ya kuma ce basu da zabi idan dai suna son ci gaba ne kuma basa son ace suna da wariya dole subi gwamna Dankwambo wajen sake bashi dama ya sake dawowa ya yi gwamna karo na biyu saboda gwamna Dankwambo, ya yi musu kokari an bai wa dansu Ministan Sufuri wanda kasafin kudin ma’aikatar sa yafi na yankin arewa maso gabas.

Sannna sai yace su mutane Gombe ta tsakiya musammam al’ummar Yamaltu Deba basa tare da wata sabuwar jamíyyar don su basa jin dari-dari ko ciwon kai balle su sha kafino ko paracitamol balle APC don haka su a yankin su PDP suka sani ba ruwansu da APC.

Da yake maida jawabi na godewa ga al’ummar jihar Gombe gwamna Dankwambo nuna fsrin cikinsa ya yi na irin hadin kai da goyon baya da suka bashi na karbar shugaban kasa a lokacin da ya ziyarci jihar a lokacin taron tattalin arzikin kasa na shiyar arewa maso gabas da ya gudana.

Daga nan sai ya yi kira na musamman ga matasa da su hada kai wajen neman abun yi don ganin sun dogara da kansu, anan ne ya yi kira da cewa su tashi su nemi keke Napep da tasi tasi da za’a bayar don samun hanyar samun abunyi su dogara da kansu.

                                                                   

                                                              xxx   

RAHOTON KAI LITTATTAFAN BASHIR OTHMAN TOFA JIHOHI BAKWAI NA AREWACIN NIJERIYA





                                                                                                                                   
11/04/2011



RAHOTON KAI LITTATTAFAN BASHIR OTHMAN TOFA
JIHOHI BAKWAI NA AREWACIN NIJERIYA

Kamar yadda aka ba wa kamfanin Gidan Dabino International alhakin tallata littattafan Bashir Othman Tofa guda takwas a jihohin arewacin Nijeriya da }asar Nijar da kuma kai littattafan zuwa ma’aikatun ilmi na jihohin domin a tallata musu don su saya. Mun fara da jihohin bakwai da kuma Yamai }asar Nijar: Ga sunanyen garuruwan:

1.     Kano
2.     Katsina
3.     Zamfara
4.     Sokoto
5.     Kebbi
6.     Neja
7.     Abuja
8.     Kaduna
9.     Zariya
10.                        Yamai Nijar

Ranar Alhamis 16/12/2010, muka fara tafiya, inda muka nufi jihar Katsina, kafin mu shiga Katsina mun tarar da ‘yan siyasa suna fa]a, ‘yan sanda kuma sun tare hanya suna ta watsa tiyagas, sun hana shiga garin Katsina, mu ma mun sha tiyagas iya rabonmu, (ni da direba Abdullahi) kuma mun tsaya carko-carko a cikin gayyar ‘yan siyasar, kafin daga baya ‘yan sanda su bu]e hanya mu shiga cikin Katsina.

Mun fara da ma’aikatar ilmi inda muka je ofishin kwamishina don isar da sa}on, amma a lokacin da muka je kwamishina bai zo ofis ba sai muka mi}a littattafan saiti guda da wasi}ar neman sayen littattafan ga sakataren kwamishinan, ya sa mana hannu a kwafin tamu wasi}ar don nuna shaidar cewa ya amshi littattafan da wasi}ar.

KVC Bookshop
Daga nan muka nufi kantin sayar da littattafai na KVC Bookshop a kan titin Yahaya Madaki, inda muka bayar da littattafan saiti 50.

Ziyara Bookshop
Sai kuma muka isa Ziyara Bookshop da ke kan titin IBB, muka ba su saiti 10. Bayan mun yi sallar magariba sannan muka nufi jihar Zamfara, inda muka kwana.

Ranar Juma’a 17/12/2010 muka je ofishin kwamishinan ilmi na jihar Zamfara inda muka bayar da littafi saiti ]aya tare da takardar neman sayen littattafan, shi ma a nan kwamishina bai shigo ofishin ba sai sakatarensa muka baiwa, ya sa mana hannu a kan kwafin wasi}armu don nuna shaidar ya amshi wannan sa}on littafi da wasi}ar.

Mai Litttafi Bookshop
Daga nan muka nufi kantin sayar da litattafai na Mai Litttafi Bookshop da ke kan titin Ahmad Bello kusa da gidan Alhaji Bala Waiman. Saiti uku kawai suka kar~a  na littafin. Sai muka nufi Sokoto don ko ma sami ma’aikata a ofis kasancewa ranar Juma’a ce.

Mun iso Sokoto daf da lokacin tafiya masallacin Juma’a, don haka muka iske ba kowa a ofishin kwamishinan ilmi, muka zauna muka jira ko za su dawo daga wajen salla amma ina, ba wanda ya dawo, don haka muka nufi masauki, (ranar dai ba mu sami sallar Juma’a ba).

Abdullahi mai Littattafai
Ranar Asabar 18/12/2010 da safe muka nufi babbar kasuwar Sokoto wajen Abdullahi mai Littattafai, wanda  muka bai wa saiti 50 na littattafan.

Sifawa Bookshop
Daga nan sai Sifawa Bookshop da ke kan titin Atiku, inda ya kar~i saiti 5 na littattafan. A Sokoto mun bar sa}on littattafan ne ga wani mutuminmu wanda ya kai mana sa}on ga kwamishina kuma ya kawo mana takardar shaidar sa}on ya isa ofishin kwamishinan, wanda PA ]in kwamishina ya amsa ya sa hannu a kan takardar ranar Litinin 20/12/2010.

Ranar Lahadi 19/12/2010 ne da rana muka nufi jihar Kebbi inda muka kwana a can. Da safiyar Litinin 20/12/2010 muka je ofishin kwamishina inda muka bayar littattafai saiti biyu saboda an nemi a yi hakan ne don a bai wa kwamishina saiti ]aya saboda wata tattaunawa da muka yi da PA na kwamishinan. Saboda wannan tattaunawar da muka yi ya sa muka da]a kwana a garin inda muka ga duk masu ruwa da tsaki wajen sayen littattafai a jihar inda muka zauna muka yi tsayayyiyar magana a kan yadda za a gudanar da wannan sayen littafi da kuma abin da za a ba su in har an saya.

Mun shiga kasuwa don bayar da tallan littafin ga wasu masu kantunan sayar da littattafai, amma abin bai yiwu ba saboda matsalar farashin ya yi musu yawa, don haka a jihar Kebbi ba mu bayar da tallan littafi ko ]aya ba.

Ranar Laraba 22/12/2010 ne da safe muka bar jihar Kebbi inda muka nufi jihar Neja, inda muka fara da ma’aikatar ilmi, muka isar da sa}on littattafan da wasi}ar, inda PA ta kwamishina ta amsa, sannan muka yi mata ]an ihsani don ta ba mu hasken lamarin kasancewar ba mu san kowa ba a wajen. Ta gaya mana yadda za mu yi don haka muka tafi wajen babban sakatare na ma’aikatar ilmi na jihar muka gaya masa abin da ke tafe da mu da kuma fatanmu, muka yi bu]a]]en zance da shi, sannan ya sanar da mu yanzu ba abin da zai yiwu sai dai bayan za~e.

KC Bookshop
Daga nan muka shiga kasuwar Gwari, inda muka je KC Bookshop, shi ne babban kantin sayar da littafin Hausa a wannan gari. Ya kar~i saiti biyu don ya jarraba ya gani don ya koka kan farashin ya yi tsada.

Ranar Alhamis 23/12/2010 da safe muka nufi Abuja, inda muka fara da ofishin babban sakatare na ma’aikatar ilmi ta birnin Abuja, ba mu same shi ba sai dai  muka bayar da sa}on ga PA ]insa, ta kuma sa mana hannu a kwafin wasi}armu shaidar ta amshi sa}on.

Ibrahim Lawal mai Aminiya
Daga nan muka nufi kusa da ofishin ABC Transport, da ke Utaka, a birnin Abuja inda muka bayar da saiti biyar ga Ibrahim Lawal mai Aminiya.

Garki Super market
Mun je kantin Garki Super market da ke Area 11, kan titin Ahmadu Bello, sun kar~i saiti 3.

Sahad Store Abuja
A Sahad Store da ke Uke Street a Garki Area 11, ba mu sami mai kula da harkar littattafai ba, sai dai mun yi waya da shi ya ce mu bar masa saiti 1 ya gwada ya gani. A ranar muka bar Abuja muka nufi Kaduna, don washegari Juma’a ce kada mu rasa samun ma’aikatar ilmi ta Kaduna.

Destiny Bookshop
Ranar Juma’a 24/12/2010 da safe muka je ma’aikatar ilmi, ba mu sami kwamishina a ofis ba, sai PA muka bai wa, ya sa mana hannu, ya kar~a. Muka kuma nemi shawarar sa ta inda za mu taro maganar, ya gaya mana, daga nan muka nufi ofishin daraktan ilmi na ma’aikatar, muka tattauna da shi, daga nan muka bar ma’aikatar muka nufi titin Ahmadu Bello, a ginin Leventis, inda muka kai wa Destiny Bookshop littattafai, ya amshi saiti 10.

Kola Bookshop
Ranar Lahadi 26 ne muka dawo gida Kano, kasancewar ranar Lahadi kantin Kola Bookshop ba sa fitowa, don haka ba mu sami ba su littafin ba a wanan karo.

Bayan mun dawo gida ne da wasu kwanaki sai aka kira ni daga Educational Resource Centre (ERC) Kaduna cewa littattafan da na kawo ma’aikatar ilmi sun iso gare su kuma suna sashen da zai duba su ya ga cancantar su da kuma inda ya kamata a karanta ko a saye su, don haka ana so in zo da }arin saiti 3, don haka }a’idarsu take, kuma za a biya ku]in duba kowane littafi 3,000, na kuma sanar da Alhaji Bashir Tofa ya yi min izini, na sake komawa Kaduna na cika wannan umarni. A wannan lokacin komawa Kaduna ne na tafi da littattafai na biya ta garin Zariya na kai wa Kola Bookshop da ke Park Road, ya kar~i saiti 5.

Edition Gashingo
Mun aika wa da kamfanin Gashingo da ke birnin Yamai ta }asar Nijar littattafai saiti 50

Al’amin Bookshop
A jihar Kano a waje daya kawai muka bayar da littafin, wato a kasuwar Sabon Gari, mun bai wa Al’amin Bookshop saiti 10, yawancin manyan kantunan da za mu baiwa an ce an kai musu, kamar Sahad da Jifatu da zamani da Country Mall, don haka ba mu kai musu ba.

Adadin littattafan da muka rarraba a kantuna da kasuwanni:
Kano:         Al’amin Bookshop  Saiti 10                                 littafi 80     
Katsina:     KVC Bookshop saiti 50                                        littafi 400
                    Ziyara Bookshop saiti  10                                     littafi 80
Zamfara:   Mai littafi Bookshop saiti 3                                   littafi 24
Sokoto:      Abdullahi mai Littafi saiti 50                                 littafi 400
                    Sifawa Bookshop saiti 5                                       littafi 40
Kebbi:        Babu wanda ya kar~a
Neja:                    KC Bookshop saiti 2                                            littafi 16
Abuja:        Garki Super market saiti 3                                     littafi 24
                    Sahad Store saiti 1                                                littafi 8
                    Ibrahim Lawan Mai Aminiya saiti 5                      littafi 40
Kaduna:     Destiny Bookshop saiti 10                                    littafi 80
Yamai Nijar: Edition Gashingo saiti 50                                  littafi 400
Zariya:       Kola Bookshop saiti 5                                          littafi 40

Jimlar littattafan da muka rabar su ne:                                 1,632

Ku]insu ya kama  Naira Miliyan [aya da Dubu [ari Shida
da Talatin da Biyu                                                                    N1.632,000

Gaba ]ayan ltitattafan da muka kar~a a wannan zagaye na farko (set 250) wato guda 2,000 ne don haka yanzu akwai sauran littattafai 368 a wajena.

Bayanai daga masu sayar da littattafai daga jihohi

Na kira mutanen da muka kai wa littattafai a dukkanin jihohin nan da kuma }asar Nijar.

{asar Nijar, abin da suka sanar da ni, lokacin da na tuntu~i manajar kasuwanci Edition Gashingo, wato Nasifa Ibrahim ta hanyar waya da kuma e-mail, ta gaya min ko littafi guda ]aya ba su sayar ba.

Abuja, Ibrahim mai Aminiya ya ce Alhamdu lillahi littafi ya samu kar~uwa ya kusa sayar da wanda ya amsa saiti 5, an sayar da Kimiyya da Al’ajuban Al}ur’ani guda hu]u N4,000, Amarzadan da Zoben Farsiyas guda ]aya N800, Amarzadan a Birnin Aljanu guda 4 N3200, Rayuwa Bayan Mutuwa guda hu]u N3200, Gajerun Labarai guda uku N3000, Mu Sha Dariya guda 4 N4000,Tunaninka Kamanninka guda uku N3,900, Kimiyyar Sararin Samaniya guda uku N4500. Jimla an sayar da litattafai guda 26, kudin su N26,600

Garki super market na yi magana da mai kula da lamarin wadda dama ita ta amshi littattafan, wato Halimat, ta ce an sayar da na N800 guda 10, an sayar da na N1,000 guda 4, na N1,300 guda ]aya, na N1,500 guda ]aya. Don haka an sayar da litattafai guda16, wanda ku]in su ya kama N14,800.

Sahad store ban sami Sulaiman mai kula da littattafan ba don haka ban ji komai game da saiti ]ayan da aka ba su ba.

Sokoto: Abdullahi mai littafi ya ce ana son littafin amma batun ku]i ne mutanen suke kasa saye, don haka ‘yan kwayoyin kawai ya sayar kamar haka: Tunaninka Kamanninka guda 2, N2600, Gajerun Labarai guda daya N1000, Mu Sha Dariya guda ]aya N1000, Amarzadan A Birnin Farsiyas guda ]aya, N800, Amarzadan Da Zoben Aljanu guda ]aya N800. Jimla an sayar da litta guda shida ku]insu N6,200.

Sifawa Bookshop ban sami magana da su ba saboda layin a rufe yake kusan duk lokacin da na kira.

Katsina: KVC Bookshop su ne suka sayar da mafi yawa, don sun sayar da set 10, wato littafi 80, wanda ku]insa ya kama N80,000.

Ziyara Bookshop ya bayyana cewa ya sayar da Kimiyya da Al’ajuban Al}ur’ani guda biyar N4,000, Mu Sha Dariya guda biyu N2000, Tunaninka  Kamanninka guda ]aya N1,300. Jimla an sayar da litattafai guda 8, ku]insu N7,300

Zamfara: Mai littafi Bookshop, ban sami layinsa ba a rufe har lokacin da na gama ha]a wannan rahoto.

Kano: Al’amin Bookshop ya bayyana min cewa an fi sayen tunaninka kamanninka, don a halin yanzu ya sayar da guda shida N7800, Rayuwa Bayan Mutuwa guda ]aya N800, Amarzadan A Birnin Aljanu guda ]aya N800, Amarzadan Da Zoben Farsiyas guda ]aya N800, Kimiyyar Sararin Samaniya guda ]aya N1,500 Kimiyyar Da Al’ajuban Al}ur’ani guda ]aya N800, an sayar da littafi guda goma sha ]aya, ku]insu N12, 500.

Neja: Ban sami magana da su ba don haka ban san halin da ake ciki ba a can sai dai nan gaba in na same su.  

Kaduna: Destiny Bookshop, sun gaya min an sayar da Kimiyya da Sararin Samaniya guda ]aya N1,500, Tunaninka Kamanninka guda uku 3,900. Jimla an sayar da litattafai guda hu]u ku]insu N5,400

Duk wa]annan wurare tuntu~ar su na yi a waya, sai Nijar da muka yi waya muka yi e-mail.

Jimlar ku]in kayan da aka sayar sun kama N152,000

SAURAN JIHOHIN DA ZA MU JE BAYAN AN GAMA ZAB|E
1.   Jigawa
2.     Bauchi                 
3.     Gombe
4.     Yola 
5.     Maiduguri  
6.     Yobe          

Wa]annan jihohi su ne sauran jihohin da za mu je don kai wa]annan littattafai ga ma’aikatun ilmi da kantunan sayarwa. Abin da ya sa ba mu yi wannan tafiya ta sauran jihohin gabacin arewacin Nijeriya ba shi ne, mun sa rana za mu tafi sai muka ji ana fa]a a jihar Gombe ana rikincin ‘Yankalare, sai muka ]aga muka ce sai wutar ta lafa. Bayan wannan ta lafa sai kuma rikici a Bauchi. Maiduguri kuwa dama ta zama fagen fama.

Daga }arshe dai muka bar tafiyar sai bayan za~e, tun da an ce turbar lafiya a bi ta da shekara, don muna zaton bayan za~en abubuwa za su yi sau}i.

Mun sanya tallan guraren da za a sami wa]annan littattafai a cikin sabon fim ]in kamfanin Gidan Dabino da ya fito kasuwa ranar Laraba 07/07/2011 mai suna SANDAR KIWO.

KARIN BAYANI
A tare da wa]annan takardu na ha]o da hoton takardun bayanin bayar da littattafan ga ma’aikatun ilmi da kuma kantuna da ‘yan kasuwa, da kuma rasitai shaidar karbar littattafan




Ado Ahmad Gidan Dabino,
Shugaba Daraktan Gudanarwa