Fagen
Siyasa
IDAN SANATAN MU DANJUMA GOJE YA KOMA APC ZAMU AIKA
TAKARDA MU DAWO DASHI----INJI Yayari
Daga
Rabilu Abubakar, Gombe
Alhaji Ahmad Yayari, Shugaban ma’aikata
ne na gidan gwamnatin jihar Gombe kuma dan asalin garin Chilo a karamar hukumar
Akko, shi ya bayyana cewa da zarar Sanatan yankinsu Alhaji Muhammad Danjuma
Goje, ya kuskura ya canja shega daga jam’iyyar PDP da aka zabe shi ya koma
jam’iyyar adawa ta APC za su tura ya dawo domin basu yake wakilta ba.
Alhaji Ahmad Yayari, ya bayyana hakan ne
a lokacin da yake gabatar da jawabinsa a garin Kumo helkwatar karamar hukumar
Akko a yayin da gwamnan jihar Alhaji Ibrahim Hassan Dankwambo, yake rangadin
ziyartar mazabun Sanatoci uku (Senatorial Tour)
A bayanan Ahmad Yayari, wanda tsohon
Kwamishina ne har tsawon shekaru takwas a tsohowar gwamnatin da ta gabatan ya
shaidawa gwamna Dankwambo cewa su al’ummar Gombe ta tsakiya musammam mutane
garin Kumo basu amfana da romon democradiyya a gwamnatin baya ba domin duk
girman garin Kumo babu aikin naira miliyan goma a shekaru takwas din da gwamnatin tayi.
Ya kuma ce koda hanyar mararabar Zambuk
zuwa Lubo da Hinna zuwa Gwani, a yankin Yamaltu Deba duk wash-wash ne akayi
yanzu ya kirayi gwamna Dankwambo da cewa ya sake su domin dai dai suke da
ba’ayi ba.
Shugaban ma’aikatan ya kara tabbatarwa
gwamana Dankwambo cewa su mutanen Gombe ta tsakiya jam’iyyar PDP suke yi kuma
tsohowar ta Bamanga Tukur, ba sabuwar ba amma Sanatan su da suka zaba Alhaji
Danjuma Goje, ya tashi a gaban duniya yace shi dan sabuwar PDP ne wanda su idan
dai a sabuwar PDP yake basu yake wakilta ba.
“
Yanzu haka muna jin rade-radin cewa zai koma jam’iyyar Hadaka wacce aka yi
hadin gambiza ta APC idan ya koma bamu
yake wakilta ba don haka gwamna ka sani amma daga ranar da muka ji ya koma APC din
mu al’ummar mazabar Gombe ta tsakiya kamar yadda muka kai shi haka zamu dawo
dashi” inji Yayari.
Ya ci gaba da cewa yanzu lokaci bai zo
tukuna amma yace suna jira suga ranar da zai koma APC din sannan kuma ya kara
da cewa mutanen Gombe ta tsakiya sun gaya masa cewa kar ya yi Magana ya zuba
ido kawai ya yi kallo suna jira suka wanda zai bada gidansa ko ofis a kafa
ofishin sabuwar jam’iyyar ta APC.
Shi kuwa Kakakin Majalisar Dokoki ta
jihar Gombe Alhaji Inuwa Garba, wanda yake wakiltar Yamaltu ta yamma cewa ya yi
su mutanen yankin Yamaltu Deba wanda take Gombe ta tsakiya bakinsu daya da
mutane Akko basa wata sabuwar jam’iyya in ba PDP ba.
Alhaji Inuwa Garba, ya kuma ce basu da
zabi idan dai suna son ci gaba ne kuma basa son ace suna da wariya dole subi
gwamna Dankwambo wajen sake bashi dama ya sake dawowa ya yi gwamna karo na biyu
saboda gwamna Dankwambo, ya yi musu kokari an bai wa dansu Ministan Sufuri
wanda kasafin kudin ma’aikatar sa yafi na yankin arewa maso gabas.
Sannna sai yace su mutane Gombe ta
tsakiya musammam al’ummar Yamaltu Deba basa tare da wata sabuwar jamÃyyar don
su basa jin dari-dari ko ciwon kai balle su sha kafino ko paracitamol balle APC
don haka su a yankin su PDP suka sani ba ruwansu da APC.
Da yake maida jawabi na godewa ga al’ummar
jihar Gombe gwamna Dankwambo nuna fsrin cikinsa ya yi na irin hadin kai da
goyon baya da suka bashi na karbar shugaban kasa a lokacin da ya ziyarci jihar
a lokacin taron tattalin arzikin kasa na shiyar arewa maso gabas da ya gudana.
Daga nan sai ya yi kira na musamman ga
matasa da su hada kai wajen neman abun yi don ganin sun dogara da kansu, anan
ne ya yi kira da cewa su tashi su nemi keke Napep da tasi tasi da za’a bayar
don samun hanyar samun abunyi su dogara da kansu.
xxx
+-+Copy.jpg)
No comments:
Post a Comment