NDE TA HORAR DA MATASA FIYE DA DARI UKU SANA’OI
HANNU DABAN-DABAN A JIHAR GOMBE
Daga
Rabilu Abubakar, Gombe
Shugaban hukumar samar da ayyukan yi kai
tsaye ta qasa NDE reshen Gombe Malam Mairiga Abdulqadir Madubi, shi ya bayyana
hakan a lokacin da yake bayyanawa wakilinmu irin aikace-aikacen hukumar ta NDE
a ofishinsa dake Gombe.
Malam Mairiga, yace amfani hukumarsu ta
NDE shine ta koyawa Matasa da Mata harma da Yara sana’oin hannu wanda zai basu
dama su dogara da kansu don su taimakawa jihar su da qasarsu dama ‘yan uwansu.
Yace a wannan shekara sun xauki Yara da
dama suna koya musu sana’oi daban-daban inda suka xauki wasu guda hamsin kuma suna
koya musu kiwon shanu da yadda zasu sarrafa abincin dabbobi da kuma yadda zasu
kula dasu wanda yanzu haka suna nan a Tiken Dabbobi na tashar Dukku, kuma an xinka musu yunifom.
Malam Mairiga Abdulqadir, yace za’a
horar da Yaran ne na tsawon watanni huxu sannan a basu bashin kuxi su fara
kiwon nasu suna saya suna kiwatata suna sayarwa suna cin riba, da haka har su
fara biyan bashin da aka basu.
Ya kuma ce yanzu haka gwamnati ta samar
da makarantu guda uku a kowanne mazavar xan majalisar dattawa da suke koyawa
Yaran sana’oi na musammam inda a Gombe
ta tsakiya suka samar da xaya a garin Daxin-kowa yankin qaramar hukumar Yamaltu
Deba, a kudancin Gombe kuma suka samar da xaya a garin Kaltungo sannan a
arewaci kuma suka samar da ita a garin Bajoga, kuma Yara dari-xari suka xauka daga
kowanne yanki.
Cikin sana’oin kuma yace akwai gyaran
naura mai qwaqwalwa Kwamfuta da koya musu gyaran wayar Salula da girke-girke da
Walda da sauransu, a cewar sa a kowacce sana’a sun xauki yara ashirin-ashirin
cikin Yara xari an rarrabasu ashirin-ashirin kenan kuma yanzu sun fi wata biyu
suna karvar horo kuma wata shida za suyi kafin ayayesu.
Sannan sai yace sun bi hanyoyin da ya
kamata wajen zaqulo yaran basu bari anyi son kai wajen xaukarsu ba saboda idan
basu sa ido ba za’a nuna son kai wajen xaukar wanda hakan bai kamata ba kuma
yace suna sawa yaran ido don ganin sun tsaya sun koyi sana’oin domin duk wanda
yake wasa bai tsaya ya koyi sana’ar yadda ta dace ba zai yi wuya su yaye shi.
Daga nan sai ya bayyana cewa idan Yaran
suka tsaya suka koyi wannan sana’oin za
suci moriyar ta domin tafi aikin gwamnati kamar yadda yace qasashen turawan da suka
ci gaba talaka shi yake aikin gwamnati kowa yafi dogara da sana’oin hannu ne wanda
sune suke vunqasa musu tattalin arzikin qasashen su.
xxx
No comments:
Post a Comment