Sunday, January 26, 2014

TATTAKI ZUWA TULA RAHOTON MUSAMMAM





RAHOTON MUSAMMAM

Garin Tula a karamar hukumar Kaltungo ya samu asali da can baya  ake kiran shi Wure- Titilo da suke da wani Kogon dutse inda ‘yan kabilar ta Tula suka yi amfani dashi wajen boye kananan Yara da Mata da Nakasassu a lokacin yakin su da abokan gaba  a shekarar 1906 inda su kuwa Matasa da Jarumai kan fito fagen daga don tarar abokan gaba.

Shi dai wannan dutse na Tula yana nan ne a garin Tula dake Yankin karamar hukumar Kaltungo dake jihar Gombe kimanin kilimita 120 daga fadar jihar, wanda yan kabilar ta Tula suka kasu gida uku Tula Yiri da Tula Baule da  kuma Tula Wange.

Wakilinmu ya yi  tattaki zuwa garin na Tula ya kuma samu ganawa da Dagacin Tula Wange Mista Andrew Aliyu mai shekaru 65 inda ya bayyana masa cewa Kakannin su suna hawa kan wannan dutse nasu don samun  kariya daga abokan gaba a lokacin yaki

Mista Andrew ya kara da cewar wannan kogon dutse da suke sanya kananan Yara da Mata a lokacin yaki kofar shigar shi karama ce amma cikin shi yana da fadi saboda kankantar kofar babu yadda abokan gaban su  a wancan lokacin zasu gane cewar mafaka ce gare su mutanen Tula.

Yaci gaba da cewar wannan kogon dutse yana daukar daruruwan jama’a kuma akwai Rijiyar da suke amfani da ita wajen shan ruwa a cikin kogon dutsen a lokacin da suke gudun hijira a ciki.

Har ila yau wakilinmu yace kogon dutsen yana da nisan Mita dari 200 ne daga mashigar garin na Tula da take kan wani tsauni, Wure Titilo dai ya kamata  ace ta zama tana daga cikin wuraren tarihi na kasa amma hakan bai yiwu ba saboda noma kawai ake yi a wajen kuma da Damina ba za ka iya gane bakin kogon dutsen ba sai a lokacin rani saboda ciyawa ta rufe wajen.

A bisa tarihin kasar Tula duk yake-yaken da suka gubza da abokan gaba babu wanda ya gudana a cikin Masarautar garin duk a waje da masarautar ya auku.

Dagacin na Tula Wange Andrew Aliyu, ya kara da cewar al’ummar Tula din sunyi yaki ma da Mutane garin Misau dake jihar Bauchi inda suka bullo da wata dabara a lokacin yakin ta hanyar gurbatawa mutane Misau din mashayar Ruwan su da guba wanda yin hakan ya basu nasarar cin su da yaki har suka cire kan sarkin Misau din suka dawo dashi garin Tula suka ajiye don tarihi.


                                                      xxxxx



No comments:

Post a Comment